Uncategorized

Abban Sojoji Chapter 11 Book 1 Complete Hausa Novel

 

“`The father Of Soldiers“`

        

Story 

     &  

       Written 

       By 

      Hafsat Bature

          (Boss Lady)

“Yanzu buri na shine, mu fara haɗa kudin zuwa wurin bokan nan, Baba Iblis domin gudanar da target ɗinmu,’ aunty babba ce ta katse ta da maganar,” .

Jiki a sanyaye Amani tace “yanzu me ake buƙata? Aunty babba tace “kuɗi nake so daga wurinki, nima kuma zan haɗa nawa don ziyartar wurinsa,

Murmushin takaici Amani tayi tare da cewa “Ita hayaam ɗin baza ta bada komai bane? 

Ƴar dariya aunty babba tayi tare da cewa “amma dai kinsan hayaam da shegen maƙon tsiya, bazata bada ko sisi ba, kuɗin ta a gantali suke karewa, mu dai taimaka mata mu yayyenta, mu yi mata inyaso in tasamu shiga wurinsa ni nasa zata ru6anya mana abunda muka kashe,’ 

Baki a sake Amani take kallonta, oh ashe tasan ma cewa Hayaam ɗin nada kuɗi, ita bazata bada ba sai dai ita gantalalliya, waye zai amfana acikinsu, 

“Yanzu nawa kke so kafin zuwa can ɗin”? Amani ta tambaya tana kallonta, cikin salon wayau Aunty babba tace “miliyan ɗaya da rabi nake so a wurinki da farko kafin abun ya nutsa,” 

Wani irin kallo Amani take binta dashi, cikin rashin fahimta tace “aunty  million ɗaya da rabi fa? daga wuri na kuma , gold ɗina kke so na siyar ne? 

girgiza kai Aunty babba tayi tare da cewa “to menene aciki ? Abbas ɗinnnan fa ya mutu akan ki, daga kin kashe masa murya buƙata zata biya,” 

Ajiyar zuciya Amani tasaki kafi  tace “I will think about it,” murmushi aunty babba tasaki acikin zuciyarta tace “ki gama yi mun aikina, ke ma nakaiki ƙasa, ƴar kishiyar da ta azabtar da mahaifiyata, tasanya mahaifina tsanata, bazata ta6a zaba ƴar uwa awurina ba face maƙiyi ya !!!” 

A fili kuma tace “yawwa my sister shiyasa nake sonki, duk cikin ƙanne na cos you’re so special,” murmushi Amani tasaki tana kallonta, 

Wannan bokan da suke magana akansa Baba iblis, wani hatsabibin boka ne fasiƙin gaske, wanda ya sharaha, Asiri kala biyu yake yi, akwai Namijin asiri wanda ƙa’ida inzaiyi sa sai ya kwanta da namiji na tsawon kwana uku yana biyan buƙata, na biyu kuma Macen asiri, idan zaiyi wannan asirin dole sai an kawo masa matar Aure wadda bata ta6a haihuwa ba ya biya buƙatarsa na 3 days, shu’umi ne nagaske, muddin yayi asiri to fa sai yaci mutun, ko yayanene, in ba wani ikon na ubangiji ba,

Kuma a haka zakaga mata na rubibun zuwa wurinsa saboda neman abin duniya, wa’iyazubillah 😥wanda kowa zai mutu yabarshi !!!!

Around two ya farka, fito wa yayi yana saukowa down, duk sun hallara a palor ɗin suna fira, jin takon tafiyarsa yasa su ɗagowa suna kallonsa, bai bi takansu ba direct bedroom ɗin Abbansu ya shiga, saboda baigansa a cikinsu ba, 

Abun da ya faru Abban nacen ɗakinsa yana zarya, shi dai burinsa Babban yaya ya kawo kansa har bedroom ɗinsa ya miƙa masa gaisuwa, if not he will not be calm, 

safa da marwa yake ta faman yi, jin tura kopa yasa shi dakatawa ya juyo yana kallonsa, tsaye yake jikinsa sanye da jallabiya fara ƙafarsa cikin slippers, ya riƙe waist ɗinsa yana kallon Abban nasu, 

Ƙinyi masa magana yayi yana jira yaga iya gudun ruwansa, shi kam kewar abban nasa yayi sosai, yama rasa wani irin tarba zaiyi masa, 

Zuba mishi ido abba yayi ganin yana naɗe hannun jallabiyar dake jikinsa kamar wanda ke shirin yaƙi, yana ganin hakan ya gane mai zaiyi masa, 

Cikin sauri yace “wlh kada kace zaka ɗauke ni Rafayet, kar ka kuskura Allah, ka matso saina nannaushe ka….” bai ƙarasa maganar ba, rafayet ɗin ya ƙarasa caraf ya ɗaga abban nasu a hannunsa kamar wani yaro, 

dariya abban ya dinga yi yana faɗin “Ka sauke ni rafayet, kada ka balla ni fa, ynx in wani ya shigo ya ganni haka fa, ‘ 

“bazan bari hakan ta faru ba abbana” cikin wata irin sanyayyiyar murya mai daɗin gaske yayi maganar, 

Ko nauyi baiji sai da ya tabbatar da cewa yaci ka abban nasu da farin ciki sannan ya sauke shi, sai faman ajiyar zuciya abban ke saki yana kallonsa, ƴar harara abban  ya watsa masa tare da cewa “duk ranar daka ƙara daukata haka, nima saina rama, kadaina ganinka da tsayi kamar fal waya , hakan bazai mun wuya ba, 

Matsawa babban yaya yayi gaf da abbansu yace”bismillah” yadda yayi masa tamkar zai rufe sa da duka, hannu abban yasa ya janyo chair ɗin dake gaban dressing mirrior , ya daddage ya hau samanta ya miƙe tsaye, yadda tsayinsa zai fi na Rafayet ɗin sosai, sbd yafi so in zaiyi masa magana yadinga ganin tsakiyar kansa, 😂

“Hmmm kayi kewata kuwa? Ni bana gane wa kullum fuska atamke ba fara’a,’ abbansu ne yayi maganar yana kallonsa daga saman chair ɗin dayake tsaye,

“Abba i really missed you just feels like to swallow you,’ yayi maganar yana kallonsa,

Shi kam abban sai murna yake yi, ba don komai ba sai don ganinsa, “amma dai zaka jima anan ko ? Bana so kana jimawa bakazo naganka ba,” 

Lumshe idonsa yyi tare da buɗesu a hankali yace”duk yadda kke so haka za’ayi abba,” murmushi abban yasaki, abun da ke ɗaure masa kai har ynx babu fara’a a fuskarsa ba alamar murmushi ko dariya, amma sanin cewa haka mood ɗinsa yake ne yasa baiji komai ba, 

“Yakamata mu fita, ku gaisa da aunty azeema da sauran ƴan uwa, kuma nasan kana buƙatar abunda zaka sawa cikin ka ko? Ya tambaya yana kallonsa,

“No am not starve dad, and i will stay here in your bedroom, duk mai son gani na yazo nan ya same ni,” 

yana gama faɗan hakan ya wuce saman bed ɗin abban nasu ya kwanta a hakimce,

Saukowa abban yayi yana murmushi aransa yace “wannan shine ainihin jinin Alexendra (alekzendira)” 

Fita abban nasu yayi fuska asake duk sun hallara a main palour ɗin ana ta fira, 

“Abba ina Babban yayan yake, nagansa ya wuce part ɗinka, nayi tunanin zan ganku atare ne,” aunty azeema ce tayi masa wannan maganar,

“You knew him well, yace duk mai son ganinsa ya same shi acan room ɗina,”  jinjina kai su kayi, aunty azeema tace “to bari muje mai son ɗan tsuntsu ae shi ke binshi da jifa,” dariya su kayi gaba ɗayansu, tashi tayi bg abuhaisam ma yabi ta tare da kanal yusif, da sauran banda su fawan,

Sun gaisa dashi sosai, anyi kewar juna asake yayi magana da kowa, amma fa face ɗin nan tashi kamar an ɗinke ta saboda rashin fara’a, 

Bayan sun fito ne abba ya kora su fawan da twins wadanda suka samu damar fito wa, munafukan hada sa jallabiya brown colour hannunsa riƙe da cazbaha,

gaba ɗaya suka tafi fawan, Ayaan da jahan dama sune basu je ba, tsayawa su kayi abakin door ɗin suka kasa shiga sbd shakkarsa,

“Enter first pls fawan,’ jahaan ne yace ma fawan, harararsa fawan yayi tare da cewa “kai ka fara shiga mana, ayaan yace “dan Allah fawan kafara shiga we’ll follow ur back pls, kowa ya gaza shiga sai faman jayayya suke yi abakin kopan ɗakin,

Duk wannan surutun da suke yi kaf a kunnan babban yayan nasu yana jinsu, sarai yasan cewa shaggun ne, ƙannensa ba, 

“Yawwa Alhamdulillah ga junaid nan shikenan ma, zo ka fara shiga,’ ayaan ne  yyi mgna with smile on his face,

Binsu da kallo junaid yyi wanda ya ƙaraso shima zuwansa kenan don ya miƙa masa gaisuwa don ɗazu yaga mood ɗinsa basu samu damar mgn ba bayan ya bude masa ƙopa, shima abban ne yasanar dashi cewa yaje ya same shi a room ɗinsa, 

“Baku da gaskiya Allah, yanzu big bro ɗin namu ne kke tsoran zuwa wurinsa, maimakon kuyi kewarsa sosai, sai faman la6e la6e ku ke…..’ 

Buge masa baki fawan yayi tare da cewa “parrot meye naka aciki, mu dallah zo ka fara shiga,” 

Shigewa gaba Junaid yayi suka bi bayansu, sai faman ƴan kame kame suke yi, sai kace ba jininsu bane shi, 

Cikin natsuwa suka ƙarasa har sun naɗe riga zasu zauna a 3 seater ɗin dake facing bed ɗin abban nasu, ya buɗe idonsa tare da yi musu wani kallo jiki na rawa suka dawo ƙasa kowa ya lankwashe ƙafa yayi zaman cin tuwo,

Haɗa baki su kayi wurin cewa “Sannu da zuwa babban yayanmu ya gajiyar tafiya,”?

Suka tambaya suna kallonsa, shiru yayi baice komai ba, zuba musu ido yayi yana kallonsu, nan fa suka soma ƴan sunne-sunnen kai,

“Is that how your mom taught u how to greet each other,!? (Haka mahaifiyarku ta koya muku yadda zaku gaisar da juna?

Ya tambaya ayayin da yake tashi zaune daga kwanciyar da yayi,

Cikin sauri suka miƙe zumbur, junaid ne ya fara ƙarasa inda yake zaune a side bed ɗin, hugging ɗinsa yayi tare da manna masa kiss a side face ɗinsa, lumshe idonsa yayi tare da jinjina kai,

fawan ma ya karasa yayi masa kamar yadda junaid yayi, haka su ayaan da jahaan ma duk suka je suka rungumesa tare da manna masa kiss,

Sannan suka koma daf dashi daga ƙasa saman carpet suna naɗe ƙafa suna jiran jin me zaice,’ 

Shi dai junaid sai faman murmushi yake don murna, ba don komai ba sai don ya gama lissafin kuɗaɗen da zai samu a wurinsa, don yaci alwashin in ya amshi kuɗi wurin big bro ɗin nasu, sai ya yi wa Sehrish ɗinsa Siyayya saboda yasan tana buƙatar abubuwa da dama, 😥

“Listening to me !! Bana so ɗaya daga cikin ku yajamin abun magana a family ɗin mu har na koma US , just i don’t wanna hear anyone saying this word again ƴa’ƴan fatima basu da kunya, if that happen you will see the trouble,’ 

Jinjina kai su kayi tare da cewa “insha Allah babban yayanmu hakan bazai faru ba, zamu kiyaye,’ 

“You can leave,’ ya basu umarni tashi su kayi jiki ba ƙwari suka fice, banda junaid wanda ya zauna yana ta faman kallonsa,” 

“What do you want from me junaid”?.

Ya tambaya yana kallonsa, murmushi junaid yasaki cikin  shagwabar nan tasa yace “akwai magana babban yaya, amma in ka huta zuwa gobe,” 

wani irin kallo babban yayan yake masa, yana son yaron sosai, duk duniya in dai har za’a samu lagwansa toh ata6a junaid nan zakaga jijiyoyin wuya, yana ji dashi more than u think,

“Ya jikin ka? kana shan maganinka akai akai,”? ya tambaya yana kallonsa,

Junaid yace “yeah am getting well, kawai nayi missing ɗinka sosai,” 

“Wow kayi missing ɗina kodai kuɗi na kayi missing, which one i have to know?

Dariya junaid yayi sosai, wato ya karto sa, tsagaita dariyar yayi kafin yace “a’a kafi mun komai mahimmanci arayuwata, kai nayi missing sosai,” 

“I miss u too junaid, sbd kai na ɗau hutu sbd inaso nabaka kulawa ta musamman game da athma ɗinka,”

Cikin jin daɗi suke firar tasu, abun gwanin ban sha’awa, sai naji kamar na tsoma baki, amma nasan naushi zansha, 😂

duk yinin ranar sehrish batasa ɗan tahalikin nan a idonta ba, saboda bai fito ba balle tagansa, in ma ya fito ɗin bata cin sa’a duk zumuɗin nan nata, 

A ranar wuraren ƙarfe 4 Aunty babba ta koma kaduna gidanta, bisa umarnin mijinta, yayin da Amani ma ta koma gidanta cike da zullumin abunda auntyn tata ta kitsa mata zasu aitawar, 

tsawon kwana 3 kennan Allah bai haɗa ta da Babban yayan ba, sai dai marshal omar da take gani da sauran da suka dawo, a yau aunty azeema ta koma lagos shima bg abuhaisam ya koma Jos inda yake da zama, 

Tara su abban nasu yayi a main palour ɗin, su 3 banda babban yayan saboda yasan maganar bata shafeshi ba, maganar zumunci ne da family ɗinsa, sam basa ga maciji da Ammi, jarababbiyar tsohuwar bata son farar fata, jinsi indai ya wuce hausa fulani ! tom sun raba jaha, har yau bata shiri da ƴa’ƴan fatima, daga abu ya faru sai tace “halan ƴa’ƴan fatima ne, ae ƴa’ƴan fatima basu da kunya, jinsin fitsararru masu jan kunne,” wannan kalmar babban yayansu ya tsane ta, bai mata da wasa in suka haɗu, gashi shegen tsoransa take ji , saboda kwayar idonsa da take blue, muddin SGR na gari to bata zuwa Abuja,’

duka suna zaune saman 3 seater wadda ke facing abbansu dake zaune yana kallonsu, gyaran murya yayi tare da cewa “Alhamdulillah nayi murnar dawowarku cikin koshin lpy , kun jima bakwa ƙasar, tun da Allah yasa kun dawo, sai ku shirya ku shiga dangi, asada zumunci !

Mg Osman ne ya fara magana “haka ya dace abba, ni inaji zan fara zuwa damaturu ne wurin modibbo da sauran relatives ɗinmu, kafin na dawo na ziyarci sauran,” 

Abban yace “hakan yayi kyau kai fa Captain ? gyara zama yayi tare da cewa “ni zan wuce kaduna ne wurin yaya ishaq daga nan zan wuce zariya ne, wurin dangi,

“Hakan yayi kyau, naji daɗi sosai amma fa yakamata asamu wanda zai je katsina wurin goggonku saboda kullum mu kayi waya sai ta tambaye ni ina, ƴa’ƴanta musamman kai Omar tafi tambayarka,” 

ɗan kayataccen murmushi Omar yasaki kafin yace *I will think about it abba*, “

Cikin jin daɗi suka ci gaba da firarsu, sai da suka washe gajiyarsu na tsawon one week sannan kowa ya shirya tafiya, marshal omar tare da Captain suka je kaduna, daga nan zasu wuce zari’a a tare, daga nan Omar ya shirya ziyartar ƙanwar amminsu da suke kira da Goggon katsina 🌹

Yau da sassafe suna kitchen suna making breakfast, azmee na tsaye agaban gas tana making suya, yayin da sehrish ke wanke kayan lambu agaban kitchen sink, ta kunna tap sai ruwa ke zuba tana wanke wa, a kasalance take yin komai, gaba ɗaya hankalinta, nakan yadda zata haɗuwa da *BABBAN YAYA* she’s so earger to see him, cos zuciyarta azalzalarta take akansa, gashi har yau batagansa ba, gashi acikin gidan amma Har yau Allah bai bata damar ganinsa ba, a ranar da suka dawo saboda ɗauki ko bacci ba tayi ba, da tunanin yadda zasu hadu ta kwana, 

Junaid ne ya shiga da kitchen ɗin da sallama, jikinsa na sanye da sleeping dress ne masu kyan gaske pink colour abun ba’a magana,

Sai xabga murmushi yake saboda sehrish daya hango, ita kam hankalin ta baya atare da ita, ta kura wa cabbage ɗin dake hannunta ido sai shafa shi take yi da sunan wanke wa,

Azmee ce tagansa ya kura wa sehrish ido, murmushi tasaki aranta tace “

*ROMEO kenan shugaban ƴan soyayya* (Romiyo) 

Kafin tayi gyaran murya tace “junaid lpy kuwa ? Do u need something?

firgit ya dawo da idonsa kan azmee wit smile on his face, yace “am…dama…..Big bro ne ke buƙatar Fresh fruits akai masa a part ɗinsa immediatly right now,’ 

Sunan sa ne ya dawo da ita daga tunanin da ta tafi, sai lokacin ta ɗago tama lura da junaid daya shigo, duk maganar da suke yi bata tsinci komai ba, sai da akai mentioning sunan Babban yaya,’ 

“Shikenan ynx zan sa sehrish ta kai masa,” sai da junaid ya sake kallon sehrish itama a lkcn idonta na akansa sannan yace “Okey” ya juya ya fice, yaji sanyi aransa daya sata a idonsa, 

Zuru tayi tana kallon azmee, murmushi azmee tayi tare da cewa “Finally sehrish wants meet Babban yaya today insha Allah,” 

Tsananin farin ciki ne ya bayyana a fine face ɗinta, murya na rawa tace “aunty azmee pls, ni zan kai masa, ni wlh tsoron haɗuwa nake da shi,” 

ta faɗi tana sunnar da kai, ƴar dariya azmee tayi tana faɗin “whether u like it or not, u don’t Ave choice, aje akaiwa big bro fruit, salon kiyi hauka, kisha mari,” 

Shirya mata tayi acikin wani ƙayataccen tray tare da knife ta yankawa ta hada mata,

Hannunta har kerma yake yi wurin amsa, sai faman mazurai take yi, har takusa fita tajuyo jiki a mace tace “Aunty azmee i don’t know  Where to find his bedroom,’ dariya azmee tayi don ta lura cewa sehrish fa a tsorace take da babban yaya, ga zumuɗin son ganinsa ga tsoransa kuwa, 

” a uptairs ne, part ɗinsa ya ke in ki ka miƙa gaba da room din junaid ba nisa,” 

jin jina kai sehrish tayi, tana tafiya zuciyarta na bugu, Just feeling nervous ta riga ta tsorata dashi, ta sama kanta tsoransa since bfr she saws him, 

a hankali take taka steps din benen, hannunta riƙe da tray din, time din da ta isa neman part dinsa ta shiga yi, sai da ta wuce room din junaid daga gaba can, ta hango wata haɗaɗɗiyar kofa, tana gani ranta ya bata cewa tabbas nan ne,

 a hankali ta yi tura door din ta shiga ciki tana wurwurga ido, lokaci guda ta rikice da ganin haɗuwarsa, wato aljannar duniya ce aka zuba aciki, parlor ne hamshaƙin gaske yaji hadaɗɗun furnitures komai na cikinsa Golden color ne , 

ko’ina sehrish ta wurga ido kyalli kawai take gani saboda haɗuwarsa, ga wasu windows na glass masu ɗaukar ido, wasu haɗaɗɗun royal sofa ne aciki  L shape, ga jerin pillows asaman su, 

bin ceilling ɗin tayi da kallo wani kwan fitila ne na zamani (chandelier) mai girman gaske sai kyalli yake kamar zai faɗo mata akai haka take ji, mutun zai iya 6ata 15 mins yana kallonsa Don kyau , daga ƙasa kuwa wasu kayattun floor lamps ne acikin glass suke masu bama wurin haske, 

mayar da idonta tayi, a saman ƙayataccen table ɗin dake a middle ɗin kujerun Container ce mai ɗauke da furanni kyawawan gaske masu tsayi sai ɗaujar ido suke, 

 Shiru tayi jugun sanyin a.c ne ke ta faman karaɗe ko’ina, tambayar kanta take yi ko nawa aka kashe wurin ƙawata wurin nan?

Wuce wa tayi ciki a hankali mamaki bai ƙare mata ba sai da ta hango wata ƙofar acikin palourn, shiga ciki tayi to fa, zamu tsaya bata baki ne, Bedroom ne ƙayataccen gaske, baki sake sehrish ke bin komai da kallo kamar a mafarki take ganin lamarin, ƙamshin ne kawai ke shiga hancin ta, ganin ba alamun mutun ne yasa ta juya wa domin ta fice,

jin alamar an buɗe kopan bathroom yasa ta juyawa taga wanene ne ?  Karaf idonta suka sauka a kansa sbd tsabar firgita tasaki tray ɗin hannunta mai ɗauke da kayan marmarin suka watse a ƙasa, zaro ido tayi waje saboda tsabagen tsoro a ruɗe take,

jikinsa na sanye da bathrobe (rigar wanka) fara mai laushin gaske, wadda ta tsaya masa dai dai guiwarsa, ya ɗaure igiyoyinta guda biyu a tsakiyar stomach ɗinsa, daga sama kana ganin wide chest ɗinsa, 

Hannunsa na ruƙe da hand towel yana matse doguwar suman kansa a natse, sam bai juyo ya kalle ta ba, amma tabbas ransa ya basa cewa wani ya shigo kuma anyi masa 6arin fruits a room ɗinsa tunda ga Apples nan guda uku ƙasan ƙafafunsa sun gangaro, ya jima yana mamakin wani isasshen ne wannan mai walkin sa, 😡

Ita kam sehrish da ke tsaye kamar gunki tarasa makama, tsantsar tsoro ne a fuskanta, dukkan ilahirin jikinta rawa yake yi sbd tsoran hukuncin da zata fuskanta, tabbas ranta ya gama yadda da cewa wannan shine Big Bro (Babban yaya) 

lips ɗintaa sai rawa suke yi hakika ta tsorata da ganin ƙirar ƙarfinsa, wannan yayiwa mutun naushi ɗaya sai dai uwarsa ta haifi wani, 

So take ta duka ta kwashe fruits ɗin da ta zubar masa a ƙasa, amma babban tashin hankalinta yadda zata ɗauko 3 apples ɗinnan da suka gangara wurin ƙafarsa 😳😳😳😳

In ka ga fuskarta sai ka tausaya mata, miyau kawai take haɗiya kut kut, yayinda zuciyarta ke buga wa da sauti mai ƙarfi, 

Har time ɗin babban yayan bai juyo ba, yana tsaye yana matse sumarsa da towel ɗin hannunsa, 

gaban dressing mirrow ya ƙarasa ya tsaya cak, ɗagowa yayi da sexy blue eyes ɗinsa ta cikin mirror yana kallon yaron dake tsaye jiki na kerma,

Allah yaso bata ɗago ta kalli cikin mirror ɗin ba, da tabbas sai tayi fitsari a wando, in tayi arba da kwayar idonsa me rikitarwa, 

gaba ɗaya komai ya tsaya cak, jiki ba ƙwari sehrish ta duƙa a hankali tana tattare abunda ta zubar, cikin gaggawa take tsince bananar da ta zubar da tufan da lemun 6awo sai tsintarsu take tana jerawa a tray ɗin, zufa na ɗiga a face ɗinta sunan Allah kawai take ambato,

Abunda bata sani ba, jira yake kawai ta ƙaraso zata ɗauki  apples ɗin dake wurin ƙafarsa yayi mata Kyakkyawan riƙo, itama ba hauka take ba a hankali take bin tufan dake wurin ƙafarsa da kallo so take takai hannu ta ɗauka, amma zuciyarta nace mata “Karki kuskura”

hawaye har sun soma wanko mata a fuska, cije wa tayi ta daure zata ɗauka har takai hannu, Junaid ya turo door ɗin yana faɗin “Am back babban yayanmu,” 

Jinsa yasa tasaki ajiyar zuciya, shima ganin sehrish ga kuma halin da take ciki yasa shi ƙarasawa da sauri yana faɗin “Let me help” 

.shiya sa hannu ya tattaro mata apples ɗin, yasa mata a tray ɗin yana kallonta duk ta firgice, 

Cikin rawar murya tace “Nasa ne aunty azmee tace na kawo masa,” 

 Ƙarba junaid ya yi tare da cewa “ok ki je kawai,” 

tana miƙa masa ko waiwaye batayi ba, ta fice jiki na rawa wato tagama rikice wa, wai a hakan ma bata ga fuskarsa da kyau ba,

Kamar wata zararriya haka ta koma kitchen din, duk tabi ta ruɗe she was amazed by his beauty, 

Kallo guda azmee tayi mata tagane cewa ba lafiya, cikin mamaki tace “Sehrish lafiyarki kuwa”? da budar bakinta sai cewa tayi “Babban yaya aunty azmee,’  wuce wa tayi gaban kitchen sink ɗin in da tabar vegetables din da take wanke wa, 

Bin ta da kallo azmee tayi tana sakin murmushi aranta tace “kaɗan kenan,”  

“Sehrish ni zan je nafara jere breakfast din a dining pls ki kular mun da farfesun dana ɗaura,sannan na manta bansanya salt ba ki zuba mun,” 

A cikin wasu haɗaɗɗun food warmers ta shirya su, ta jerasu a saman faffaɗan tray ta fice don tafara jerawa, 

sehrish sam bata farimtar komai still she’s out of sense , ita dai taji kamar tace ta zuba gishiri, 

Cikin rashin sani tasanya Hannu ta ɗauki Ledar detergent, bil’haƙki da gaske taje  ta bude murfin sauce pot (tukunyar miya)  dake a saman gas, ta zazzage sa duka kaf Aciki , ta kuma ɗauki turner tana motsawa, gaba ɗaya hankalinta nakan surar babban yaya da ta gani, ta mutukar jan hankalinta, 

bakomai idonta ke hasko mata ba fa ce wannan doguwar sumar kan tasa mai dan bala’in kyau, 😳😳😳

Shigowa azmee tayi tana fadin “kinsa mun gishirin aciki “? jin muryar azmee yasa ta dawo daga tunanin da take yi, sai lkcn ta ankara da ledar detergent ɗin da ta zazzage acikin farfesun wadda ke a ƙasa,  a razane ta dafa ƙirji tana fadin “Nashiga ukuna, wayyo Allah wlh omo na zuba maimakon gishirin !!!? 

Sakin baki azmee tayi tana kallonta, jinjina kai kawai take yi, tana jinjina wa lamarin, sehrish kuwa ido yayi luhu luhu duk ta kame kanta,

“Sannu kin ji ? Azmee ta fadi tana kallonta, sunnar da kai ƙasa tayi tana fadin “am so sorry aunty azmee sharrin shaidan ne ba yin kaina bane,’ 

Azmee tace “sharrin shaiɗan kuma ko dai sharrin babban yaya wanne ciki? cije le6enta kawai take yi itama tarasa meke damunta,

“U did a good job sehrish, u need to ave some rest, aikin ki ya ƙare, sai da anjima in kin dawo hayyacin ki,’ cikin sanyin murya tace “dan Allah aunty azmee kiyi hkr, nasan fushi ki kayi dani, I made a big mistake am so sorry, bazan kara ba” 

Murmushi azmee tayi tace “sam ni baki 6atamin rai naba, hasalima tausayin ki nake ji, Je ki huta,’ 

Kama hanya sehrish tayi ta fice daga kitchen ɗin tana mamakin haukanta na yau  akan big bro, (nace ba saura na anjima ko na gobe) 😂

Sehrish bata dawo cikin hayyacinta ba sai da tayo wanka, tasamu natsuwa sosai, a gefen gadonta tazauna tana ta faman zabga murmushi, farat ɗaya taji wani irin yanayi atare da ita, har takai ga ko runtse ido tayi shi take gani sanye cikin bathrobe, a tunaninta jinsa yafi ganinsa ashe ganinsa yafi jinsa nesa ba kusa ba, hannu tasanya ta janyo fillow ta kwantar da jikinta a saman gadon, idonta na kallon ceilling, 

*tabbas shiɗin burin kowace ƴa mace ne 💋

*Baki washe an samu dinner 😂*

………………..*………………………

~Husanna & Jahad~

Ƙanƙame suke da junansu A cikin Cell ɗin, cikin mawuyacin hali, sun rame sunyi baƙi, haƙiƙa sun ga rayuwa, yanzu an kammala shirya komai na shigar dasu kotu domin gudanar da shari’a A next week,

ƙarar bude cell ɗin suka ji, da sauri suka ɗago, wata jami’a ce sanye cikin kakin ƴan sanda, mai riƙe da muƙamin inspector, 

su biyu ne ita da wani jami’i amma ita kaɗai ta shigo ciki, zuƙunnawa tayi gabansu tana binsu da kallo fukarta cike da tausayinsu,

a tsorace suke kallonta, baka ce babu annuri a fuskarta sai manyan tsaguna a fuskarta na rumawa, 

“Idan zaku bani haɗin kai zan taimake ku, ku fita daga haɗarin da kuke ciki,” ta faɗi tana kallonsu

 Cikin sanyin murya Jahad tace “komai kike so zamuyi dan Allah ki taimake mu mubar wurin nan, mun gaji, bamu ji daɗin zama anan, kuma bamu so akwai mu kotu a yanke mana hukuncin kisa,” ta kare maganar idonta cike tab da kwallo, 

Murmushi inspector eesha tayi kafin tace “tabbas zaku fita, amma bisa sharaɗin in muje kotu zaku amsa cewa kune ku kayi kisan batare da jayayya ba !!!?

Zaro ido jahad tayi tana fadin “sabod me ? taya zamu ansa hakan bayan bamu ne muka kashe ta ba “?

shiru inspector ɗin tayi tana kallonta, da alama yarinyar zatayi taurin kai,

Husanna dake kanƙame gefen jahad tace “Ni na amince zan ce ni nasanya mata shinkafar 6era taci ta mutu, indai zaki fidda mu dan Allah,” 

“Husanna !!! kada ki kuskura ki amince wlh ni banyarda ba wlh,” 

Jahad ce tayi maganar tana kallon fuskar jami’ar, wadda tabisu da ido,

“Wlh ni na amince dan Allah aunty ki fidda mu, zance ni nayi kisan indai zaki cika alƙawari, 

hannu jahad tasa ta rufe mata baki daƙarfi tana cewa “amma sai yau na tabbatar baki da hankali husanna wlh bazan bari hakan ta faru ba sbd we’re not guilty, ‘ 

ganin sun soma ƙoƙarin ɗaga murya yasa ta dakatar dasu da cewa “You have to trust me, ni turo ni akayi na taimake ku kuma dole sai ta wannan hanyar,

Cikin mamaki Jahad tace “wa”?

Murmushi tayi kafin tace “daga wurin ƴar uwarku SEHRISH,”

Jin ta ambaci sunan sehrish yasa su gyara zama suna masu tsananin mamaki,  wani irin farin ciki ne ya bayyana a fuskarsu, 

“Dan Allah dagaske ne sehrish zata taimake mu ? dama tasan halin da muke ciki ne, Allah ne ya amshi addu’ar mu zamu fita daga wannan uƙubar,” 

 Jahad ce tayi maganar da tsantsar farin ciki aranta, husanna kam sam tagaza rufe bakinta murya na rawa tace “Dama nasani Sehrish bazata bari a cutar damu ba, nasan tana son mu sosai, dan Allah a fiddamu daga nan akaimu wurin ƴar uwarmu,” 

Kallansu kawai inspector ɗin take yi, wani irin kallo na shu’umanci ganin sun miƙa wuya yasa tace “kun amince zaku amsa cewa kune ku kayi kisan!!”?

Atare suka haɗa baki wurin cewa ehh mun amince,’ 

ƴar dariya tayi kafin ta fita daga cell ɗin, a  harabar police station ɗin ta tsaya jikin motarta, hannu tasa a aljihun wandonta ta ɗauko wayarta ƴar nokia, daddanawa tayi kafin ta kara a kunnanta tare da cewa  “Yaran fa sun amince, zasu amsa cewa sune su kayi kisan, yaushe zanji alert na cikon kuɗi na ?

Natsuwa tayi tana sauraron mutumin da ta kira a waya, wanda ba’a bamu damar jin me yake cewa ba,

Dariya inspector ɗin tayi kafin tace “nima fa shu’uma ce kamar kai, muddin banji alert ba na cikon kuɗi na, ina mai tabbatar maka da cewa, zansa su fasa amsa laifin,’ 

Ta jima tana wayar kafin ta kashe wayar tana tikar dariya (to fa)

A can cikin cell ɗin kuwa, wani tunani ne yazo ma Jahad ita mai hankalin taya akai ƴar sandar nan tasan sunan sehrish !!!!? Kuma taya akai Sehrsh tasan halin da suke ciki ? Tabbas akwai makirci acikin lamarin, 

Miƙewa tsaye tayi tana zagaye, can dai tace “husanna so ake mu amsa laifin kisan nan don akashe mu, ba don ataimake mu ba !!

jiki a mace husanna tace “jahad ni nagaji da rayuwarnan, so nake na mutu kuma yanzun nan,!!

hankali atashe jahad tayi hanzarin komawa kusa da ita tazauna tare da dafa shoulder ɗinta tace “Husanna bakya jin daɗi ne,” 

“Eh mutuwa zanyi yanzun nan,” 

ta bata amsa, bin ta da kallo jahad tayi a tsorace ganin , jini ya soma biyowa ta hancinta, daga magana sai abu ya tabbata, kafin ta ankare husanna ta zube ƙasa, ba numfashi,

Wata irin razananniyar ƙara Jahad tasaki tare da faɗin “Innalallahi wa’inna ilaihirraji’una !!! Nashiga uku !!Wayyo Allah na Husanna ta mutu………..

da gudu police ɗin dake waje suka shigo ciki, sun gigita da ganin halin da yarinyar take ciki tamkar ba numfashi, kuma sun son tabbas ta mutu a hannunsu sai anji dalili,

hakan yasa aka kira women police  guda biyu suka ɗauki husanna, hada jahad aka tafi da su cikin mota domin kaita asibiti, 

Sai faman kuka Jahad take kamar ranta zai fita saboda tana ji aranta cewa Husanna fa wannan karon dakyar zata rayu,

Ganinsu da ƴan sanda yasa, reception nurses saurin karbarsu, aka shiga da husanna ciki a (A&E) accident and emergency ward aka kwantar da ita, 

nan da nan likitoci suka shiga duba ta, Jahad na zaune a saman waiting seats dake daga waje Ward din, tasha kuka ido sunyi jawur, 

Ga ƴan sanda zagaye da su,kamar wasu 6arayi, addu’o’i kawai take karantowa abakinta , tana roƙon Allah yasa Husanna karta rasa ranta, tsananin ƙunci ne a ranta, kuma tasawa ranta cewa muddun *Husanna* ta mutu itama sai ta kashe kanta ❗‼⁉, 😭😭😭

Domin Sauke Cikakken Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now!

……………….SEHRISH…………………………

Back to top button