Novel Document

Boddiya Complete Hausa Novel Document – Aihausanovels

BOƊƊIYA Complete Novel Document

Written By:
Aisha Sani Abdullahi
*(Xayyeesherthul-humaerath)*

_Hi, Hello, Fans😍Gani na dawo da wani labari mai ɗauke da nishadantarwa, ilimantarwa ……. ba ma sai na ce komai ba,ku kun sani kuma zaku bada labari, Kafin in ci gaba da Series din Yel na ce bari mu taɓa wanan,kada ku bari a baku labari domin labarin na musamman cikin musamman dinma na daban ne_

*Note: littafina na kudine, 300 kacal*

Bismillahir-Rahmanir-Rahim

Gabadaya baya cikin hayyacinsa tuƙi yake ba tare da duban hanya ba,duk da kasancewar dare ne kuma ga duhu,motoci sun kauracewa titi sai shi kadai yana watangaririya.

Kamar ance ya kalli gabansa, cikin sauri ya taka burki ganin yadda idanunsa ke nuna masa tamkar mutumne kwance gabansa.
Ƙara motsa idanunsa ya yi da hannu domin tabbatar da abun da zuciyarsa ke aiyana masa.
Tabbas Mutum ne,ya furta a kasale,jiki ba kwari ya fito, fitowar da zaiyi kuwa gabansa ya yi mummunan faduwa ganin yarinyar da baza ta zarce shekara goma ba kwance cikin jini,ga dukkan alamu ta galabaita ta ko wani bangare,tallafota ya yi,yana kara kallon gaba da bayansa,babu shakka ba kowa a wannan titin a yanzu kam,to amman taya….
Ya gagara karasa furtawa kokarin dagata ya fara yi, ba karfi jikinsa amman haka ya jata a hankali yasa a mota sannan ya ci gaba da tuƙi cikin sauri.
Yana isa gida ya fara Horn Tamkar mala’ikan da aka turo daukan rai da sauri mai gadin ya bude masa ya shiga.

Fitowa ya yi a motar kamar zai faɗi yana fadin.
“Ga,,ga wata nan shigo da ita ciki.”

Bai kara fadin komai ba ya shige kawai.

Kasancewar mai gadin yasan halinsa sarai ba tsaya tambaya ba kawai ya shiga cikin motat tare da ɗaukan yarinyar, shi kan shi sai da ya tsorata ganin yarinya karama cikin wani yanayi ga jini duk jikinta.

“Oh Allah ko meya faru kuma, Allah sa dai ba kasheta ya yi ba.”

Yana fada tare da daukanta ya shiga da ita,a falo ya ajeta kan kujera sannan ya fito.

Shi ko Dr Rowan kwanciya ya yi barcin minti goma kafin ya tashi ya shiga wanka ganin ya dawo hayyacinsa yasa shi karasawa gareta, fara cire mata fingilin zanin ya yi abun da ya kara bashi mamaki shine tabbatar da cewa anyiwa yarinyar fyaɗe ne.
Tsaki ya yi yana fadin, “Oh My God! Wai yaushe za abar hakewa kanun yara hakane? Yanzu shi wanda ya yi wannan aikin me zai ji anan?”
Tsaki ya yi, yana shiga cikin bedroom dinsa, fitowa ya yi da first aid box a hannunsa ya mata dukkanin abun da ya dace harda allurar barci sannan ya dauketa ya je toilet ya wanke mata jiki tas tare da sanya mata wata rigarsa a jiki ya kwantar da ita.
Kayanta kuwa zubarwa ya yi a shara tukun yaje ya kwanta shi ma.

Cikin dare ya ji an farka ana kurma uban ihu,da maimakinsa ya buɗe ido tare da kunna wuta  domin shi ya ma manta da batun akwai wata yarinya a gidan.

Ita ko ta dage ban da ihu ba abun da take kurmawa tana fillanci.

“Hey Stop, ki yi shiru ki koma ki kwanta ba kisan yanzu dare bane?”

Maganar da yake tamkar yana kara zugata ihu ta kara yi tana kuka tare da kankame jikinta musamman yanayin dakin da ta lura da shi wanda ko a mafarkinta bata taɓa cin karo da shi ba,bare kuma a zahiri.

Karanta>>> Abban Sojoji Page 60 Book 2 Complete Novel

Ga shi ,shi kansa ma bata taba ganin mutum mai yanayi irin nasa ba adoron duniya.
Kallon da ta kara masa a karo na biyu ne ya kara tarwatsa mata kwakwalwa ganinsa sanye da fararen kaya.

Ba tantanma ta mutune, nan ba duniya bane, rufe ido ta yi da hannayenta jiki na rawa tana ƙara,motsa jiki take son yi da niyar ta tashi ta gudu ko zata bar wannan lahirar amman ina gaba-daya ta kasa motsawa jikinta ciwo yake ta kowanni bangare.

Wata irin gigitacciyar tsawar da Rowan ya yi mata ne ya bata nutsuwa cikin second guda tare da sake wani mawuyacin fitsari.

Ya lura sam ba jin yaren da yake yi take ba daga turancin har hausa hakan ya sa shi sakin tsaki tare da shiga toilet ya yi alwala ya kama sallar dare.

Ita kuwa tunani ta fada, shin wacce duniya ce wannan ta tsinci kanta a ciki da ko maganar mutanen ciki ba ta ji, ga shi komai nasu ya banbanta da wanda ta saba gani anata duniyar illa abu ɗaya da ya bata mamaki yana sallah kamar yadda ta baro tasu duniyar ana yi kuma har ita ma tana yi,amman bayan nan komai ya banbanta,kanta ne ya fara mata wani jarababben ciwo ta dafe ,kuka kuwa ta kasa yinsa a zahiri domin ji take in ta kara wani motsi mai kara zai iya cinyeta.

Karanta>>> Wace ce ita (Who is she) Complete Hausa

Zuba masa idanu kawai tayi yana sallah tana kallo har barci ya kara kwashe ta ba tare da ta ankare ba.

Gari ya waye,motsin Rowan da ta ji ne yasata fara buɗe ido a hankali.

Wanka ya yi yana shirin sa kaya hankalinsa kwance yana taje gashin kansa.

Kashi ta fara ji tana so ta yi magana amman bata san me za ta ce ba,ga shi ya matseta ,a zuciyarta take rayawa, “Daman a wannan duniyar ma mutum na jin kashi kamar yadda muke yi a duniyarmu?”

Kara cikinta ya fara yi yana kurari alamar tabbas kashi ne yake shirin fitowa nan take ta sake wata irin tusa da shegen wari tamkar miyar kukan da tai wata guda a ajiye.

Hada ido sukai nan take tana zaro ido shi ma yaiy tsuru dukaninsu ba su san me zasu cewa juna ba domin ko sun yi magana babu mai fahimtar wani.

Kuka kawai ta kara fashewa da shi,yayin da ka………………

Domin Sauke Cikakken Littafin sai ku danna inda aka saka Download

Back to top button